Wasu sukan shiga damuwa bayan sun bayyana sirrin
zuciyarsu a wajen mace kuma yazamana basu samu karbuwa ba a wajenta ba , dalilai biyu suke sa
mace taki amincewa da namiji, na farko shine idan Allah bai hada jininku ba,
indai Allah bai hada jininku da yarinya ba duk abunda zakayi bazaka burgeta ba.
Abu nabiyu wani dalili ko matsala ce daga gareka yasa bata son ka, ko baka iya
saka kaya ba ko baka iya Magana ba da dai sauransu.
·
Idan ka bayyana wa mace kana sonta bata
amince dakai ba sai ka tsaya ka duba daga ina matsalar take? Abubuwan dazaka
duba sune lokacin da zaka je gurinta wani irin kaya kasaka? Mata nason gayu
suna son samari yan gayu, idan kayan daka saka daza fara zuwa wajenta bamasu
kyau bane to sai ka duba wanan ga gyara.
·
lokacin dakake magana da’ita zaka fahimci
idan bata jin dadin maganarka ko kuma kana fadan wani abu wanda yake bata mata
rai, to dole ka canza salon maganarka zuwa yanda ka tabbatar zataji dadinsa.
·
Atakaice dai ka lura da ta’ina matsalar
take idan daga kaine sai ka gyara ka sake salo watakila ta karbeka.
·
Idan kuma ka fahimci matsalar badaga kai
bane kawai itace dai bata sonka ko kuma tana da wani wanda take so, to idan
kayi iya kokarinka sai ka hakura ka kyaleta kawai kanemi wata, indai yarinya ta
nuna bata sonka abinda yafi kawai ka hakura sabida zaka zama kana ta shan
wahala akanta ita kuma bata yabawa. Ka hakura ka nemi wata akwai mata dayawa
watakila wata ma tana sonka takasa gayamaka.
No comments:
Post a Comment