Babban dan kasuwa kuma hamshakin mai kudi kuma wanda
yafi kowa kudi a Africa wato Alhaji
Aliko Dangote, yace yana da shirin sake
aure domin ya zauna ya huta kaman yanda kowa yake.
Alhaji Aliko Dangote ya bayyana cewa shekarunsa a
yanzu sunkai sittin (60) shiba yaro bane ya kuma nuna cewa harkokinsa ne na
kasuwanci suka hanashi ya zauna da matan daya aura, yace bai kamata ka ajiye mataba
alhali bakada lokacinta.
Dangote dai yace bayan ya kammala aikin gina matatar
man fetur dinsa zai yi aure ya huta.
Tini dai aka samu wasu mata dasuka nuna cewa sufa sun
dade suna kaunarsa kuma a shirye suke a daura aure, shin kana ganin wanan so ne
nagaske ko akwai ayar tambaya?
No comments:
Post a Comment