Hawaye sun zubo a fiskar Shugaban kasa Muhammadu
Buhari a jiya lokacin da yakai ziyara ta jaje akan gobarar data tashi a kasuwar
Azare dake Jihar Bauchi wanda tayi sanadiyar konewan shaguna dasuka kai 750.
Shugaba Muhammadu Buhari |
Shugaba Buhari yakai ziyarar ne domin ganewa idonsa
barnar da asarar da gobarar ta jawo a kan yan kasuwan.
Shugaba Buhari yace gobarar dai kaddara ce daga Allah,
kuma ya jajantawa yan kasuwan sannan ya tabbatar da cewa Gomnatin tarayya
zatayi iya kokarinta wajen taimakawa wadanda abun ya shafa.
Gwamnan Jihar Bauchi, Muhammad Abubakar da Sarkin
Katagum, Alhaji Umar Faruk sun nuna godiyarsu da ziyarar da Shugaba Buhari ya
kawo musu.
Sarkin Katagum, Allhaji Umar Faruk, ya nemi taimakon
gomnatin tarayya wajen kara inganta tsaro a hanyoyin Azare – Potiskum sabida
yawan fashi da akeyi a hanyar.
No comments:
Post a Comment