Friday 8 June 2018

Abinda Buhari yace zaiyi wa matasa



Shugaban kasa Muhammadu Buhari yace gomnatinsa tana kokarin shawo kan matsalolin matasa da sauran matsolin dasuka damu kasar baki daya, yayi wannan jawabi ne a yau daya karbi bakoncin kungiyar matasa da kuma yan kungiyar wasa na fim da sauransu a taron shan ruwa wanda fadar shugaban kasa ta gayyacesu.

Shugaban ya kara da cewa gomnatinsa na kokarin kyautata rayuwar matasa ta bangarori daban daban yanda zasu tsaya da kafafunsu har su samu daman daukan wasu aiki. Yace Gomnatinsa zata cigaba da kawo hanyoyi da zasu inganta.

Shugaba Buhari ya bawa matasan shawaran suci gaba da neman ilimi a kowani mataki domin cigabn al’umma.


Shugaban ya kuma jaddada muhimmanci na wayarwa da yan kasa hankali akan yin katin zabe musamman da lokacin zabe yake karatowa.

A yayin jawabinsa a madadin kungiyoyin, Mr Kunle yayi godiya ga shugaba Buhari sabida kokarinsa wajen habaka tattalin arzikin kasa da kuma cigaba ga al’ umma kuma yayi alkwarin jagorantan matasa wajen nuna goyon bayansu ga Gomnatin shugaba Buhari domin cigaban kasa.


No comments:

Post a Comment