Jarumi Adam zango babban jarumi ne wanda indai kana
maganan sanaar film na Hausa dole sai kayi Magana akanshi, jarumi ne a masana'antar film ta kannywood wanda ya
bada gudumawa sosai a cikin masana’antar ta fim din hausa wato Kannywood. Wanan
jarumi bai tsaya a fitowa cikin fim ba kawai yakasance yana shirya fim kuma
yana bada umarni. A bayan harkar fim
jarumi Adam Zango yana wakoki na hausa wanda yafi karfi a wakokin gayu, kuma
yana wakoki da rayuwa da fadarwa da sauransu.
Akwai labarai dayawa da aka wallafa akan Adam Zango da
rayuwarsa da iyalansa a shafuka dayawa wanda wasu sun kasance gaskiya wasu kuma
ba gaskiya bane, a wanan zamuyi bayani akan tarihi da iyalai da rayuwar Adam
Zango.
Takaicaccen
tarihin Adam Zango
Asalin sunan Adam Zango shine Adamu Abdullahi kuma an
haife shi a daya (1) ga watan oktoba shekara ta 1985 a garin Zango dake jihar
Kaduna. Adam zango yafara ne da kida da waka na hausa wanda yake hada ta yanayi
na gayu wanda ake kira hausa hip-hop wanda a wancan lokacin kusan shi kadai
yake wanan, hakan yasa yasamu farin jinni sosai ganin ya kawo abunda babu shi.
Ganin yanda abubuwa suka cigaba Adam zango ya yanke
shawarar shiga harkar fim, Adam zango yafara fim ne a matsayin karamin jarumi, Adam
zango bai dade da fara fim ba yasamu karbuwa sosai a wajen masu kallon fim din
hausa har yazamana ana hada shi da manyan jarumai na kannywood irinsu Ali Nuhu
da dai sauransu.
![]() |
Photo credit: Daily Trust |
Iyalan
Adam Zango
Adam Zango ya auri matarsa tafarko a shika dake Zaria
dake jihar Kaduna, sunanta Aisha kuma sun haifi yara dayawa tare da Adam Zango.
A shekara ta 2013, Jarumi Adam Zango ya auri jarumar
da ta fito a fim din NAS, wato Maryam Abdullahi Yola a lugbe dake garin Abuja.
Amma kafin auren Jaruma Maryam Abdullahi, anyi hira da
Adam Zango inda ya bayyana cewa yanada wata matar kafin auren Aisha hakan
yanuna cewa Adam Zango ya auri wata matar kafin Aisha.
A shekara ta 2015, Adam Zango ya auri wata yar kasar
Kamaru mai suna Ummu kulsum. Aurensa da Ummu kulsum yakasance sirri wanda
yabawa masoyansa dakuma sauran yam fim mamaki ganin yanda abun yakasance a boye
babu wanda yasamu labari, sun sami haihuwar ya mace da ummu kulsum wanda aka
saka mata suna Murjanatu.
Adam Zango ya auri mata dayawa, wasu daga cikin
abokanan aikinsa ma sun bayyanna cewa basu san adadin yawan matan daya aura ba.
Mujallar Fim magazine ta bayyana cewa Ummu kulsum
itace matarsa ta karshe kuma da ita suke tare a yanxu. Anga hotunan su da shi
daita da jaririyarsu a shafukan sada zumunci na jarumin, hakan ya jawo cece
kuce dayawa.
No comments:
Post a Comment